IQNA

'Yan Gudun Hijirar Rohingya Na Fuskantar Matsaloli

18:00 - September 20, 2017
Lambar Labari: 3481916
Bangaren kasa da kasa, musulmi masu gudun hijira 'yan kabilar Rohingya suna fusnkantar matsaloli a wuraren da suke a cikin kasar Bangaladesh.
Kamfanin dillancin labaran iqna ya bayar da rahoton cewa, musulmi masu gudun hijira 'yan kabilar Rohingya suna fusnkantar matsaloli a wuraren da suke bayan sun tsere daga muhallansu.

Babbar matsalar da suke fusnkanta it ace ruwan sama wanda ke zuba kamar da bakin kwarya a cikin yankunansu da suka baria cikin kasar Myanmar, hakan nan kuma a kan hanyarsu ta zuwa kasar bangaladesh da ke makwaftaka da wurin.

Da dama daga cikinsu suna yin amfani da ledoji domin kare kansu daga ruwan sama, wanda kuma hakan baya wadatarwa, yayin da wasu kuma sukan mutu a cikin koramu da suke tsallakawa.

Yanzu haka rahotanni sun tabbatar da cewa akwai adadi mai yawa na mutanen da suka mutu a cikin koramu, wasu kuma a kan hanya sakamakon kamuwa da cututtuka ko gazawa.

3644232


captcha