IQNA

‘Yan ta’adda na Daesh a Iraki Sun Kashe Babban Limamin Masallacin Mausil

23:49 - June 14, 2014
Lambar Labari: 1417545
Bangaren kasa da kasa, yan ta'adda sun yi wa malam addinin musulunci yankan rago a birnin Musil a ranar Alhamis da ta gabata, da suka hada har da babban limamin birnin Sheikh Muhammad Mansuri, wanda daya ne daga cikin manyan malaman Ahlu-sunnah a kasar, saboda yaki ya yi musu mubaya'a, kamar dai yadda iyalansa suka tabbatar.

Kamfanin dillancin labaran Iqna ya habarta cewa, 'yan ta'addan alka'ida sun yi wa malam addinin musulunci goma sha biyu yankan rago a birnin Musil da ke arewacin kasar a ranar Alhamis da ta gabata, da suka hada har da babban limamin birnin Sheikh Muhammad Mansuri, wanda daya ne daga cikin manyan malaman Ahlu-sunnah a kasar, saboda yaki ya yi musu mubaya'a, kamar dai yadda iyalansa suka bayyana ga manema labarai.
A wani labarin kuma Kakakin rundunar sojin kasar Iraki kanar Kasim Al-ata ya fadi yau cewa, daga jiya Juma'a zuwa yau Asabar, kimanin matasa miliyan daya da rabi ne suka kai kansu a sansanonin sojin kasar, domin daukarsu aikin soji na sa-kai domin yaki da 'yan ta'addan alka'ida, ya ce yanzu haka an fara ba su horon gaggawa.
Yayin da anata bangaren kungiyar malaman Ahlu-sunnah a kasar Iraki (Jama'at Ulama Al-Iraq) ta fitar da fatawa a yau Asabar, inda ta halasta daukar makami domin yaki da 'yan alka'ida a kasar. Shugaban kungiyar Sheikh Khalid Almulla shi ne ya karanta sanarwar a yau.
1417407

Abubuwan Da Ya Shafa: Iraq
captcha