IQNA

15:38 - September 12, 2025
Lambar Labari: 3493857

Majalisar Dinkin Duniya ta yi Allah wadai da harin da Isra'ila ta kai kan Qatar

IQNA - Kwamitin Sulhu na Majalisar Dinkin Duniya ya fitar da wata sanarwa inda ya yi Allah wadai da hare-haren da gwamnatin haramtacciyar kasar Isra'ila ke kai wa Qatar.

Majalisar Dinkin Duniya ta yi Allah wadai da harin da Isra'ila ta kai kan Qatar

 jiya mambobin kwamitin sulhu na MDD sun yi Allah wadai da hare-haren baya-bayan nan da Isra'ila ta kai a birnin Doha fadar mulkin kasar Qatar, tare da yin kira da a kawo karshen tashe-tashen hankula a yankin.

A cikin sanarwar da kwamitin sulhun ya fitar, mambobin kwamitin sun bayyana matukar damuwa a kan mutuwar fararen hula a wadannan hare-hare.

Sanarwar ta kuma jaddada muhimmancin kawo karshen tashe-tashen hankula da kuma goyon bayan diyaucin kasar Qatar.

A karshen sanarwar, mambobin majalisar sun sake jaddada goyon bayansu ga muhimmiyar rawar da Qatar ke takawa a kokarin shiga tsakani a yankin.

A ranar Talata, 9 ga watan Satumba, gwamnatin Isra'ila, a wani mataki da ba a taba gani ba, ta kai hari kan ofisoshin shugabannin Hamas a Doha; wani mataki da ya haifar da tarzoma a matakin yanki da na duniya. Jami'an Qatar sun bayyana harin a matsayin wanda ya sabawa dokokin kasa da kasa da kuma ayyukan ta'addanci, sannan kuma da yawa daga cikin kasashen yankin sun yi Allah wadai da shi.

 

 

4304555

 

 

captcha