Kamfanin dilalncin labaran Iqna ya habarta cewa, ya nakalto daga shafin sadarwa na ayanr gizo na Sadal Balad cewa, ministan kula da harkokin addini na Masar ya ce cikin shekara mai zuwa a gudanar ad shirin da kur'ani da nauinsa da suka hada da bangaren gajiyarwa ta kur'ani tare da kore bayan da ke cewa an hana yin hakan baki daya a fadin kasar.
Tun kafin wanann lokacin ana bayyana mahukuntan masar da danne hakkokin malamai, kamar yadda aka bayyana kasar Masar a matsayin daya daga cikin kasashen da ake take hakkokin ‘yan jarida. Jaridar kasar Masar da ake bugawa da harshen trance ta buga cewa; a cikin shekaru uku na bayan nan adadin ‘yan jaridar da aka kashe sun kaisha daya.
Har ila yau jaridar ta kara da cewa; kawo ya zuwa yanzu yawancin mutanen da su ke da hannu a kisan ‘yan jaridar ba a gurfanar da su a gaban kotu ba domin su fuskanci shari’a. Jaridar ta kuma ambato jami’an kare hakkin bil’adama na kasar suna yi kira ga mahukunta da su dauki matakan gaggawa domin bada kariya ga ‘yan jarida da kuma hukunta masu cin zarafinsu.