Cibiyar koyar da Alkur'ani ta Iran Iqna bayan ta nakalto daga majiyar Aljazira net ta watsa labarin cewa: a cikin wannan makala Saruj Halimi mai nazari dan asalin kasar Labanon ya rubuta cewa: hukumomi na kasa da kasa bas u nuna da gasket suke ban a hukumta shugabanni da komandodin sojin Haramtacciyar Kasar Isra'ila da suka tabka leifukan yaki a harin da suka kai wa Gaza.Wannan mai nazari dan Faransa mai shekaru 61 a cikin wannan makala ya jaddada cewa: sojin Isra'ila sun ruguza da dama daga cikin cibiyoyi da gidajen da aka gina su da dukiyoyin kasashen kungiyar tarayyar Turai kuma adaidai wannan lokaci kungiyar tarayyar Turai bat a maida martini ko sau daya ba.
Saruj Halimi a cikin makalar ya yi tunatarwa da cewa : majalisar dokoki ta Amerika ta kare ta'addancin Isra'ila ka Gaza ta hanyar fitar da kudurin cewa Isra'ila tana kare kanta net a hanyar kisan gilla da gare dangin fararen hula a Gaza. Wannan lamari na nuni da rashin adalcin Yammaci musamman Amerika mai kare manufar Haramtacciyar kasar Isra'ila ta kawar da Hamas.
359373