IQNA

Wani Mamba A Jihadul Islami Ya Soki Isra'ila Kan Wuce Gona Da Iri Kan Masallacin Quds

8:29 - February 25, 2009
Lambar Labari: 1748317
Bangaren kasa da kasa: Wani jagora a kungiyar jihadul islami nafiz Azzam ya yi kakkausar suka kan Isra'ila dangane da wuce gona da iri da take yi kan masallacin Quds mai alfarma.
Kamfanin dillancin labaran ikna ya nakalto daga kamfanin dillancin labarai na (Ma'an) cewa; a wata zantawa da ta hada shi manema labarai yau a Gaza, Nafiz Azzam daya daga cikin jagoroin kungiyar Jihadul Islami, ya bayyana cewa Isra'ila tana wuce gona da iri a kan masallacin Quds, wanda kuma hakan nauyi na day a rataya kan musulmi da larabawa, da su dauki dukkanin matakan da za su iya wajen kawo karshen barazanar da masallacin Quds ke fuskanta daga daga Isra'ila.
A bangare guda kuma ya soki shiru da wasu bangarori na larabawa da musulmi ke yi kan tabargazar da Isra'ila take aikatawa a birnin Quds da ma sauran yankunan Palastinawa.

368983


captcha