IQNA

Kungiyoyin Kare Hakkin Bil Adama Na Kasashen Musulmi Za Su Gudanar Da wani Zama

11:09 - February 26, 2009
Lambar Labari: 1748770
Bangaren siyasa: Kungiyoyin kare hakkin dan adam za su gudanar da wani taro kan halin da palastinu ke ciki, domin daukar matakan shari'a kan Isra'ila.
Kamfanin dillancin labaran Ikna ya nakalto daga shafin internet na ma'aikatar shari'ar Iran cewa; , bisa la'akari da cewa batun Palastinu da kuma halin al'ummar palastinu suke ciki musamman bayan kai hare-haren ta'addancin da Haramtacciyar Kasar Isra'ila ta kai kan alummar Gaza, ya zama wajibi kungiyoyin lauyoyi da masu kare hakkin bil adama na kasashen musulmi su gudanar da zama, domin daukar matakan da suka dace wajen gurfanar da Haramtacciyar Kasar Isra'ila a gaban kotun manyan laifukan yaki ta duniya, bisa laifukan yakin da ta tafka kan fararen hula a Gaza.
Bayanin ya ce za a gudanar da zaman a mako mai kamawa.

369384

captcha