IQNA

Cibiyar Hukunce-Hukuncen Musulunci Ta Yi Allawadai Da Cin Cin Zarafin Annabi (SAW)

13:13 - March 03, 2009
Lambar Labari: 1751102
Bangaren kasa da kasa: Sakataren cibiyar kula da hukunce-hukuncen musulunci ya yi kakkausar suka dangane da cin zarafin manzon Allah (SAW) da gidan talabijin din Isra'ila ya yi.
Kamfanin dillancin labaran Ikna ya nakalto daga jaridar (alhayat) ta kasar Saudiyya cewa; A wani bayani da sakataren cibiyar hukunce-hukuncen musulunci ya fitar, yabayyana cewa tozarta matsayi manzon Allah da tashar talabijin Isra'ila ta yi a cikin wani shirinta, ba shi ne karo na farko day a hudawan sahyuniya suka yi hakan ba, domin kuwa wannan aiki ne da tarihi ya tabbatar musu da shi, inda suka shahara da tozarta annabawan Allah. Bayanin ya ce taba manzon Allah (SAW) taba addinin musulunci ne da musulmi baki daya.
Bayanin ya yi kakkausar suka kan wannan wannan mummunan aiki na tasahar talabijin din Isra'ila, kamar yadda bayanin ya yi Alladawai da wani shiri makamancin haka da tashar ta watsa, wanda ya ci zarafin annabi Isa (AS) da Maryam (SA) mahaifiyarsa.

371566
captcha