Cibiyar da ke kula da harkokin kur'ani a Iran Ikna ta nakalto majiyar tabarai ta Nasij cewa: kungiyoyin musulmi da na kiristoci masu kira da goyan bayan kare masallacin kudus sun isar da sako da bukatarsu na kare masallacin daga hannun makiya da kuma kubutar da shi daga hannun azzalumai Yahudawan Sahayoniya da cewa sojojin haramtacciyar kasar isra'ila sun yi shekaru sun ci gaba da mamaye wannan masallaci da kuma garuruwan Palasdinwa amma a bangare daya shugabannin Larabawa sun yi gum da bakinsu da hakan ke bayyana cewa: yahudawan sahayoniya da su babu wani bambanci saboda haka kungiyoyin suke kira da bukatar larabawa da su kawo karshen wannan zalunci da Palasdinwa da Masallacin Kudus ke gain daga makiyansu yahudawan sahayoniya.
381722