IQNA

Rashin Adalcin Da Ya Mamaye Duniya A Yau Yana Takurwa Sauran Kasashe

13:38 - April 07, 2009
Lambar Labari: 1761553
Bangaren siyasa: shugaban tawagar majalisar dokokin Iran a taron hadin gwiwa da aiki tare a tsakanin majalisun kasashen duniya ya bayyana cewa; a yau yanayin da duniya ke ciki ana danne hakkin al'ummo da rashin adalci day a mamaye duniya.
Bayan ta nakalto da majiyar labarai a majalisar dokoki ta Iran ,cibiyar da ke kula da harkokin kur'ani a Iran Ikna ta watsa rahoton cewa:Hashmatullah Falahat Pisha mamba a komitin tsaro ada siyasar harkokin waje a majalisa a matsayinsa na shugaban tawagar Iran a wajen taron hadin gwiwar majalisun dokokin duniya ya bayyana cewa: yau shekaru da dama duniya na fama da rikice-rikice na rashin adalci kuma a kullum sai lamarin kara muni yake yi. Kuma Ya kara da cewa yanayin da ake ciki a yau lamarin sai kara muni yake yin a nuna danniya da zalunci a fili .har ila yau ya ci gaba da cewa matukar ba a dauki mataki ba cikin gaggawa to ba a san abin da zai faru a nan gaba ba domin babu wani hakki da ake karewa ko ake kiyaye wa musamman na marassa karfi da su ne suka fi fama da wannan matsala a fili karara.

383737

captcha