Kamfanin dillancin labaran Ikna ya nakalto daga bangaren kula da taruka na jami'ar mazhabobin musulunci da ke Iran cewa; : an bude taro a jami'ar mazhabobin musulunci da ke birnin Tehran, domin yin nazari dangane da mahangar Imam Khomeini kan juyin juya halin muslunci, wanda kuma taron na hadin gwiwa ne tsakanin jami'ar da kuma ma'aikatar ilimi. Bayanin ya ci gaba da cewa a wajen taron an yin sharhi ne kan wasu littafai ko laccoci na Imam da suka shafi juyin juya halin musulunci, inda a kan bayyana mahangar Imam tare da yin sharhi kan hakan. Taron dai yana samun halartar masana daga sassa daban-daban na kasar Iran gami da daliban jami'a da suka rubuta makaloli kan hakan.
389082