Bayan da jaridar Alshaiba da ake bugawa a kasar Oman ta kawo labarin ,cibiyar da ke kula da harkokin Kur'ani a Iran Ikna ta watsa labarain cewa;cibiyar da ke kula kula da yada al'adun musulunci ta sarki Kabus na kasar Oman ta fara karbar sunayen duk wanda yake son shiga da damawa da shi a cikin gasar karatun kur'ani a wannan kasa.Sai dai wani hamzari ba gudu ba duk wanda ya kasance bai taba cin wata lambar yabo ta karatun kur'ani ta kasa da kasa ba shi da damar shiga wannan gasa .Wannan yana daga cikin sharadin babban da wannan kasa ta yi gindaya ga duk wanda yak e son shiga wannan gasa.
389123