IQNA

Ya Kamata Masar Ta Fahimci Hadarin Da Ke Fuskantar Duniyar Musulmi Daga HKI

16:15 - April 21, 2009
Lambar Labari: 1768093
Bangaren siyasa: kakakin ma'aikatar harkokin wajen Iran bayan da babban sakataren kungiyar hadin kan kasashen musulmi ya bayyana aniyarsa ta taimaka wajen shiga tsakani na magance matsalar da ke faruwa na zargin da kasar Masr ke yi .
Cibiyar da ke kula da harkokin kur'ani a Iran Ikna ce ta nakalto daga bakin kakakin ma'aikatar harkokin wajen Iran Hasan Kashkawi na bayyana cewa ya kamata kasar Masar ta fahimcin irin barazanar da ke fuskantar kasashen musulmi a yau daga gwamnatin haramtacciyar kasar Isra'ila.Kuma ya zama dole kuma wajibi gwamnatin kasar Masar ta daidaita harkokinta da sauran kasashen musulmi a maimakon ta ci gaba da zarginsu a kai akai da yi wa gwamnatin haramtacciyar kasar Isra'ila hidima babu ji babu gani da hana isar da duk wani taimako zuwa ga yan uwansu musulmi kuma larabawa a yankin gaza.

391451
captcha