Kamfanin dillancin labaran Ikna ya nakalto daga kamfanin dillancin labaran APS cewa, ministan ma'aikatar kula da harkokin ilimi mai zurfi na kasar Senegal Mostapha Sourang ya bayyana cewa; za a gina jami'ar ne a garin Dianiadio, kamar yadda za a gina wata makarantar sakandare ta musulunci a Keur Massar da ke kusa da birnin Dakar fadar mulkin kasar. Ya ce ma'aikatar kula da harkokin addini ta kasar Saudiya tare da hadin gwiwar ma'aikatar kula da harkokin ilimi mai zurfi ta kasar Senegal za su gudanar da aikin tare, kuma yanzu haka bangarorin biyu sun fara gudanar da aikin kamar yadda aka tsara.
393551