Kamfanin dilalncin labaran ikna ya habarta cewa; Kasashe goma sha hudu ke alkalanci a gasar karatun kur'ani mai tsarki da ake gudanarwa a birnin kualalmpur na kasar Malazia. Bayanin ya ci gaba da cewa babbar cibiyar kula da harkokin kur'ani ta sarki fahad ita ce ta dauki nauyin gudanar da wannan taro, inda aka fitar da wasu daga cikin muhimman kayan tarihi da ke bayyana fasahar addinin musulunci tun tsawon shekaru sama da dubu daya da suka gabata. Taron yana samun halartar masana dake gudanar da bincike kan wasu muhimman abubuwa da suka shafi tarihin musulunci, daga cikin kasar da ma wajen kasar.
444316