Kamfanin dillancin labaran Iqna ya nakalto daga kamfanin dillancin labaran Dunya habar cewa; Musulmin kasar Jamus sun bukaci da a bas u hutun ranakun idin karamar salla da bababr salla, domin raya ayyukan addininsu da ake gudanarwa a wadannan ranaku. Bayanin ya ci gaba da cewa yanzu haka babbar cibiyar kula da harkokin addinin muslunci ta kasar Jamus ta mika takardun da ke neman gwamnatin Jamus, bayanin ya ci gaba da cewa ana sa ran gwamnatin Jamus za ta amince da wannan nema. 479153