Kamfanin dillancin labaran iqna ya habarta cewa Babban editan jaridar kasar Brazil ta Folha ya bayyana cewa; al'ummar Brazil suna da matukar sha'awar sanin addinin Musulunci da koyarwarsa. Bayanin ya ci gaba da cewa editan jaridar ta Folha ya bayyana hakan ne a tarukan baje kolin kayan sadarwa da ake gudanarwa a nan birnin Tehran, wanda ke samun halartar kafofin yada labarai daga sassa daban-daban na duniya. 483452