Bangaren kasa da kasa; Musulmin kasar Norway na gudanar da wani zaman taro kan yadda ya kamata a magance matsalolin rayuwar zamantakewa a kasar, musamman ma tsakanin iyalai da dangi na al'ummar kasar baki daya.
Kamfanin dillancin labaran iqna ya nakalto daga shafin internet na icenews cewa; Musulmin kasar Norway na gudanar da wani zaman taro kan yadda ya kamata a magance matsalolin rayuwar zamantakewa a kasar, musamman ma tsakanin iyalai da dangi na al'ummar kasar baki daya. Bayanin ya ci gaba da cewa babbar manufar gudanar da taron ita ce kara kusanto da fahimtar juna tsakanin iyalai, sakamakon rashin jituwa da kan tsanani tsakanin iyalai a kasar ta Norway a wannan lokaci. 497064