IQNA

An Gudanar Da Bincike Kan dangantakar Musulmi Da Kiristoci Na Etiophiya A Tsawon Tarihi

16:10 - February 17, 2010
Lambar Labari: 1887346
Bangaren al'ada da Fasaha: an gudanar da bincike da nazar kan dangantakar da ke tsakanin musulmi da kiristoci a tsawon tarihin kasar Etiophiya wato Habasha.
Cibiyar da ke kula da harkokin kur'ani a Iran Ikna ce ta watsa labarin cewa: an wallafa da watsa wani bincike da ya kumshi shafuffuka saba'in da takwas da kuma ofishin yada al'adun kasar Iran a wannan kasa ta Etiophiya ya dauki dawainiyar da nauyin tabbatar da wannan aiki. Wannan bincike da nazari ya kumshi bangaren tarihi na mazhabobi a wannan kasa ,bayyanar Musulunci da kirsitoci a wannan kasa da kuma dangantakar Musulunci da kiristoci a mahangar Musulunci da kuma gajeran tarihin dangantakar bangarorin biyu a matsayinsu na manyan addinan Allah a wannan kasa. Sai kuma dangantakar musulmi da kiristoci a mahangar dokokin wannan kasa a hukuma mai ci .

539437
captcha