Cibiyar da ke kula da harkokin kur'ani a nan jamhuriyar Musulunci ta Iran Ikna daga jamhuriyar Azarbaijan ta watsa rahoton cewa; yan sanda a jamhuriyar Azarbaijan duk da cewa suna kula da tsaro da ayyukan da wahabiyawa ke gudanarwa a masallacin Abubakar da ke birnin Baku sun kuma dakatar da ayyukan wahabiyawan a wannan masallaci.Kamat Suleiman Uf Babban malamin Wahabiyawa day a yi karatun addini a kasar Saudiya kan wannan labari ya bayyana cewa; kofar masallacin ta jima a rufe kuma yan sanda bas u barin wani ya shiga cikin masallacin sai dai a yan kwanakin nan suna lura da masallacin baki daya.
562464