Kamfanin dillancin labaran iqna ya habarta cewa, shafin sadarwa na ilknokt ya habarta cewa, an fitar da wani littafi na wakokin yabon manzon Allah (SAW) a cikin harshen turkanci, wanda wani mawakin classic na kasar Mahmud Kapalan ya rubuta. Rahoton ya ce tun bayan da addinin muslunci ya yadu a dukkanin sassan da daular Usmaniyya ta shimfida karfin ikonta, 'yan kabilar turk sun yi ta kokari a bangarori daban-daban domin yada addinin muslunci,daga cikin kuwa hard a rubuta littafai da kuma rubuta wakoki daban-daban da ma wadanda ake rerawa, da suka hada da na wayar da kai da kuma na yabon manzon Allah (SAW) a cikin harshen turkanci. 597219