IQNA

Wakilan Cibiyar Addinai Ta Turkiya A Baje Kolin Kur'ani

17:31 - August 25, 2010
Lambar Labari: 1981460
Bangaren kasa da kasa; Mutane hudu ne daga cikin wakilan cibiyar addinai ta kasar Turkiya suka halarci baje kolin kayayyakin kur'ani mai tsarki da ke gudana a birnin birnin Tehran fadar mulkin jamhuriyar Musulunci ta Iran.


Kamfanin dillancin labaran iqna ya habarta cewa, wasu mutane hudu ne daga cikin wakilan cibiyar addinai ta kasar Turkiya suka halarci baje kolin kayayyakin kur'ani mai tsarki da ke gudana a birnin birnin Tehran, wanda kuma shi ne karo na goma sha bakawai da ake gudanar da irin wannan baje kolin kur'ani na kasa da kasa a birnin.

Bayanin ya ci gaba da cewa, wakilan cibiyar addinai ta kasar Turkiya ta bude wani daki a wurin baje kolin, inda kawo wasu daga cikin ayyukan fasaha da musulmin kasar Turkiya suka yi na ado da rubutun kur'ani mai tsarki.

640418


captcha