IQNA

Za A Kafa Kwamitin Hadin Gwiwa Tsakanin Musulmi Da Kiristoci A Masar

17:44 - January 04, 2011
Lambar Labari: 2058987
Bangaren kasa da kasa, Za a kafa wani kwamitin hadin gwiwa tsakanin mabiya addinin kirista da kuma mabiya addinin Musulunci a kasar Masar da nufin samar da zaman lafiya da fahimtar juna tsakanin dukkanin mabiya addinan biyu.


Kamfanin dillancin labaran iqna ya habarta cewa, a wani labari da ya nakalto daga shafin sadarwa na yanar gizo na Muhit an bayyana cewa, za a kafa wani kwamitin hadin gwiwa tsakanin mabiya addinin kirista da kuma mabiya addinin Musulunci a kasar Masar da nufin samar da zaman lafiya da fahimtar juna tsakanin dukkanin mabiya addinan biyu da ke zaune a kasar.

Rahoton ya kara da cewa babbar manufar kafa wanna kwamiti ita ce haifar da yanayi na zaman lafiya da kuma kawo karshen tashe-tashen hankula tsakanin mabiya addinan biyu, musamman ma a cikin 'yan lokutanan, lamarin da ya fuskanci Allawadai daga malaman addinin muslunci.

A cikin watan decemban da ya gabata an kai wasu hare-hare kan majami'oin mabiya addinin kirista a Masar, kamar yadda aka kai wasu makamantansu a lokacin da suke bukin sabuwar shekarar bana.

723227
captcha