Bangaren kasa da kasa, za a gudanar da wani zaman taro na karawa juna sani kan juyin juya halin Musulunci a Iran a birnin London fadar mulkin kasar Birtaniya, wanda zai samu halaratar masana daga sassa daban-daban na kasar da za su gabatar da jawabai.
Kamfanin dillancin labaran iqna ya hbarta cewa, a wani labari da ya nakalto daga shafin sadarwa na yanar gizo na ic-el an bayyana cewa, za a gudanar da wani zaman taro na karawa juna sani kan juyin juya halin Musulunci a Iran a birnin London fadar mulkin kasar Birtaniya, wanda zai samu halaratar masana daga sassa daban-daban na kasar da za su gabatar da jawabai ga mahalarta taron.
Juyin juya halin Musulunci a Iran ya zama wata babbar matashiya ga musulmin da suka gafala kan addininsu da koyarwa, inda ya raya ruhin Musulunci da tunanin juyi a tsakanin al'ummar musulmi ta duniya, daga cikin alamun tasirin juyin kuwa har da yadda wasu mabiya addinai kan kawo ziyara a kasar kuma suke karbar addini.
Za a gudanar da wani zaman taro na karawa juna sani kan juyin juya halin Musulunci a Iran a birnin London fadar mulkin kasar Birtaniya, wanda zai samu halaratar masana daga sassa daban-daban na kasar da za su gabatar da jawabai.
746041