Bangaren kasa da kasa, babban jagoran mabiya mazhabar shi’a na kasar Bahrain Ayatollah Shikh Isa Kasim ya yi kakkausar suka kan kisan gilla da mahukuntan kasar Bahrain suke yi wa masu gudanar da zanga-zangar cikin ruwan sanyi domin bayyana ra’ayoyinsu na siysa da suka hada da hakkokinsu da ake dannewa.
Kamfanin dillancin labaran iqna ya habarta cewa, a wani labari da ya nakalto daga shafin sadarwa na yanar gizo na ya akausar cewa, babban jagoran mabiya mazhabar shi’a na kasar Bahrain Ayatollah Shikh Isa Kasim ya yi kakkausar suka kan kisan gilla da mahukuntan kasar Bahrain suke yi wa masu gudanar da zanga-zangar cikin ruwan sanyi domin bayyana ra’ayoyinsu na siysa da suka hada da hakkokinsu da ake dannewa daga bangaren mahukuntan kasar.
Shehin malamin ya yi wannan kakkausar suka ne a lokacin da yake gabatar da hudubar sallar juma’a a masallacin Imam Sadiq (AS) da ke garin Al-diraz na kasar Bahrain, inda ya ya kira ga mahukuntan kasar Bahrain da su yi amfani da hankali wajen warware koke-koken da mutane suke yi a kasar maimakon daukar matakan yin amfani da karfin tuwo wajen murkushe zanga-zangar da fararen hula suke gudanarwa.
Babban jagoran mabiya mazhabar shi’a na kasar Bahrain Ayatollah Shikh Isa Kasim ya yi kakkausar suka kan kisan gilla da mahukuntan kasar Bahrain suke yi wa masu gudanar da zanga-zangar cikin ruwan sanyi domin bayyana ra’ayoyinsu na siysa da suka hada da hakkokinsu.
750045