IQNA

Musulmin Indiya Sun Yi Jerin Gwanon Nuna Adawa Da Kisan Kiyashi Kan Al'ummar Bahrain

19:44 - March 29, 2011
Lambar Labari: 2098874
Bangaren siyasa da zamantakewa:musulmi a garin Lakhunu a jiya lakwas ga watan farvardin shekara ta dubu daya da dari uku da tisi'in hijira shamsiya sun gudanar da wata zanga-zangar lumana da a ciki suka fito fili suka nuna adawa da takaici da kuma Allah wadai da yadda ake yi wa al'ummar kasar Bahrain kisan kiyashi.


Kamfanin dillancin labarai na Ikna da ke kula da harkokin kur'ani a nan jamhuriyar musulunci ta Iran ya watsa rahoton cewa; musulmi a garin Lakhunu a jiya lakwas ga watan farvardin shekara ta dubu daya da dari uku da tisi'in hijira shamsiya sun gudanar da wata zanga-zangar lumana da a ciki suka fito fili suka nuna adawa da takaici da kuma Allah wadai da yadda ake yi wa al'ummar kasar Bahrain kisan kiyashi.Wannan zanga-zangar hukumar tabbatar da sulhu ce ta shirya kuma a jawabin da hujjatul Islam Said Amir Haidar Radawi ya bayyana cewa; Amerika ita babbar makiyin musulmi kuma a yau ya zama wajibi kuma dole musulmi su magance sabani da bambance-bambancen da ke tsakaninsu don haka ya bas u dama baki daya murkushe zalunci.

766628

captcha