Bangaren kasa da kasa, an fara zaman tattaunawa tsakanin kasashen musulmi da kuma kasashen yammacin duuniya abirnin Abu Dhabi na kasar hadaddiyar daular larabawa, da nufin samun fahimtar juna a kan lamurran da suke da sabanin mahanaga a kansu kan harkoki na kasa da kasa.
Kamfanin dillancin labaran iqna ya habarta cewa, a wani labari da ya nakalto daga shafin sadarwa na yanar gizo na WAM an bayyana cewa, an fara zaman tattaunawa tsakanin kasashen musulmi da kuma kasashen yammacin duuniya abirnin Abu Dhabi na kasar hadaddiyar daular larabawa, da nufin samun fahimtar juna a kan lamurran da suke da sabanin mahanaga a kansu kan harkoki na kasa da kasa, da kuma wadanda suka shafe su kawai.
A wani labari da ya nakalto daga shafin sadarwa na yanar gizo na cm-life an bayyana cewa, za agudanar da wani zaman taro na yin nazari kan fasahohin muslunci na zamani, wanda aka shirya gudanarwa jami’ar Machigan, da jami’an gami malamai daga jami’ar d akuma wasu jami’oin kasar Birtaniya za su samu halarta, da ma wasu kasashen ketare.
Wasu rahotannin kuma sun yi nuni da cewa mabiya addnin muslunci na kasar Italia musamman ma mazauna birnin Rom, suna ganin cewa bisa la’akari da yawan da suke da shi a kasar, daidai da ddokokin da aka amince da su auna da ahakkin su mallaki babban masallacin juma’a a cikin birnin Roma, kuma sun aike da takardun neman izini kan hakan, amma har yanzu mahukunta ba su ce komai ba. 793317