IQNA

Kungiyar Hizbullah A Lebanon Ta Yi Allawadai Da Keta Alfarmar Kur'ani Mai Tsarki

17:06 - February 23, 2012
Lambar Labari: 2279466
Bangaren kasa da kasa, kungiyar gwagwarmayar muslunci ta hizbullah a kasar Lebanon ta yi kakkausar da yin Allawadai da keta alfarmar kur'ani mai tsarki da sojojin mamayar Amurka suka yi a kasar Afghanistan tare da kone shi.

Kamfanin dilalncin labaran iqna ya habarta cewa, ya naklato daga shafin sadarwa na yanar gizo na tashar talabijin din Almanar cewa, kungiyar gwagwarmayar muslunci ta hizbullah a kasar Lebanon ta yi kakkausar da yin Allawadai da keta alfarmar kur'ani mai tsarki da sojojin mamayar Amurka suka yi a kasar Afghanistan tare da kone shi domin tsokanar musulmi.
A kalla mutanen 10 ne suka rasa rayukansu a kasar Afganistan a ci gaba da zanga zangar nuna fushi kwanaki ukku a jere wanda mutanen kasar daga bangarorin daban daban suke yi don keta hurumin Al-Qur'ani mai girma wanda sojojin mamaya suka yi a barikin Bagram a ranar litin da ta gabata.
Akalla mutum guda ne ya rasa ransa a yau Alhamis sannan wasu 4 kuma suka ji rauni, biyu daga cikinsu yansanda ne, a lardin Baglan.
Yau ne kwana ta ukku a jere wanda yansanda kasar Afganistan suke kokarin dakatar da zanga zangar nuna fushi wanda mutanen kasar ta Afagnistan suke yi kan kona al-kur'ani mai girma wanda sojojin mamaya suka yi.
A ranar litinin da ta gabata ce wasu sojojin mamaya da ke Sansanin sojojin NATO a Bagram suka kona wasu littafan addini daga cikinsu har da wasu kofi kofi na Al-Qur'ani mai girma.
A zanga zangar jiya laraba dai mutane kimani 9 suka rasa rayukansu a yankunan daban daban da kasar ta Afganistan kan wannan lamarin.
958164
captcha