Bangaren kasa da kasa; shugabannin kungiyar gwagwarmaya ta musulunci ta neman yantar da Palasdinu Hamas sun bayyana cewa: A yau ne ashirin da watan Ordebehesht na shekara ta dubu daya da dari uku da tis'in hijira shamsiya a wani babban taro da za a gudanar za a tabbatar da matsayi da tarihi mai inganci na Palasdinu da rubuta shi cikin manyan bakake.
Kamfanin dillancin labarai na ikna da ke kula da harkokin da suka shafi kur'ani mai girma a nan jamhuriyar musulunci ta Iran ne ya watsa rahoton cewa: shugabannin kungiyar gwagwarmaya ta musulunci ta neman yantar da Palasdinu Hamas sun bayyana cewa: A yau ne ashirin da watan Ordebehesht na shekara ta dubu daya da dari uku da tis'in hijira shamsiya a wani babban taro da za a gudanar za a tabbatar da matsayi da tarihi mai inganci na Palasdinu da rubuta shi cikin manyan bakake.An nakalto daga majiyar labarai ta CPI cewa; shugabannin kungiyar gwagwarmaya ta Hamas za su gudanar da wani gagaramin taro na nuna tarihin Palsdinu kuma a gurin wannan taro za a samu halartar Isma'il Haniya zaben firaministan yankin Palasdinu da al'ummar Palasdinu suka zaba har ila yau kuma za a samu halartar wakilai da kungiyoyi da hukumomi da mu'assisoshi a yankin Gaza na Palasdinu.
1002734