Bangaren kasa da kasa, masu tsananin kiyayya da addinin muslunci a kasar suna ta kara tsananta kai hare-hare a kan masallatai da cibiyoyin addinin muslunci da ke kasar a mwani mataki na tsokana wanda suka rika dauka a lokutan baya inda har sukan kai hari kan kabrukan musulmi.
Kamfanin dillancin labaran iqna ya habarta cewa ya nakalto daga shafin sadarwa na yanar gizo safir news cewa, masu tsananin kiyayya da addinin muslunci a kasar suna ta kara tsananta kai hare-hare a kan masallatai da cibiyoyin addinin muslunci da ke kasar a mwani mataki na tsokana wanda suka rika dauka a lokutan baya inda har sukan kai hari kan kabrukan musulmi wqanda hakan ya samo asali daga mulkin da ya gabata.
A can kasar Azarbaijan kuwa wasu daga cikin musulmin kasar da suke da masaniya kan harkar yanar gizo sun shiga cikin wasu shafuka mallakin gwamnatin kasar da take tsananin gaba da addinin musulunci suka bata su a wani mataki na mayar da martani kan matakan takurawa ga mabiya addinin muslunci.
A wani labarin kuma an bayyana cewa wannan jam’iya tan ada manufofi na siyasa da suka yi daidai da mahnarta, ta yadda take son saka addini ya zama shi ne ma’anu a cikin dukaknin lamurranta na siyasa, haka nan kuma idan ta samu karbuwa a wajen al’ummar kasar tana sa ran za ta kawo gagarumin canji.
‘Yan siyasa da wasu daga cikin masana da kuma malamai sun kafa wata jam’iyar masu kishin islama a kasar Libya wanda shi ne karon farko da hakan ta kasance wadda ta kwashe shekaru arba’in da biyu karakshin mulkin kama karya na tsohon jagoran kasar.
1010604