IQNA

Masu Ra’ayin Kishin Musulunci A Jordan Suna Zanga-Zangar Neman Sauyi

21:51 - May 27, 2012
Lambar Labari: 2335461
Bangaren kasa da kasa, wasu daga cikin masu kishin islama na kasar Jordan sun gudanar da wata bababr zanga-zanga a biranan kasar domin neman a gudanar da garanbawul a cikin harkokin siyasa da mulkin kasar tare da neman a kawo karshen cin hanci da rashawa.
Kamfanin dilalncin labaran iqna ya habarta cewa ya nakalto daga shafin sadarwa na nayar gizo na jaridar Al-rayi ta kasar Jordan cewa, masu kishin islama na kasar Jordan sun gudanar da wata bababr zanga-zanga a biranan kasar domin neman a gudanar da garanbawul a cikin harkokin siyasa da mulkin kasar tare da neman a kawo karshen cin hanci da rashawa da ya yi katutu a kasar.
A can birnin Alkahira dubban mutanen kasar Masar ne suka gudanar da zanga-zangar yin Allawadai da keta alfarmar kur’ani da aka yi a kasar Amurka tare da yin kira da adauiki matakin korar jakadan kasar Amurka da ke zaune a birnin Alkahira saboda rashin saukar matakin da ya dace na kare alfarmar musulunci a kasar.
Wani bangare guda kuma an gudanar da wani babban taron cika shekara guda da samun nasarar juyin juya hali a kasar Masar wanda ya kai ga kifar da gwamnatin kama karya ta tsohon shugaban kasar Husni Mubarak daga mulkin kasar ta Masar a jiya.
Bayanin ya ci gaba da cewa wannan babban taro ya kayatar matuka, bisa la’akari da cewa kasar Masar tana da matukar muhimamnci a cikin kasashen larabawa da kuma yankin nahiyar Afirka baki daya, wannane ma ya sanya yanzu haka kasashen larabawa da suke yin amshin shata ga siyasar turawa.
Rahotannin sun tabbatar da cewa, dubban daruruwan mutanen ne suka gudanar da wani babban taron cika shekara guda da samun nasarar juyin juya hali a kasar Masar wanda ya kai ga kifar da gwamnatin kama karya ta tsohon shugaban kasar Husni Mubarak daga mulkin kasar ta masar mai dogon tarihi.
1016783






captcha