Bangaren kasa da kasa, adadin masu amfana da kayan abinci na Halal yana matukar karuwa a kasar Faransa a cikin lokutan nan lamrin da ke nuni da cewa masu natsuwa da addinin muslunci a cikin harkokinsu na yau da kullum da cinikayya suna karuwa a kasar duk kuwa da tsananin gaba da mahukuntan kasar ke yi da muslunci.
Kamfanin dillancin labarn iqna ya habarta cewa ya nakalto daga shafin sadarwa na yanar gizo na Promise Consulting cewa, adadin masu amfana da kayan abinci na Halal yana matukar karuwa a kasar Faransa a cikin lokutan nan lamrin da ke nuni da cewa masu natsuwa da addinin muslunci a cikin harkokinsu na yau da kullum da cinikayya suna karuwa a kasar duk kuwa da tsananin gaba da mahukuntan kasar ke yi da muslunci musammn ma a lokacin gwamnatin da ta gabata.
A jiya an gudanar da wani zaman taro na tunawa da shahadar Imam Musa Kazim (AS) a birnin London na kasar Birtaniya wanda cibiyar kula da harkokin musulunci ta kasar ta dauki nauyin shryawa da gudanarwa tare da halartar malamai da kuma masana daga ko’ina cikin fadin kasar.
Majalisar mabiya addinin muslunci a kasar Faransa za ta shigar da kara kan mutanen da suek nuna matuar adawa da addinin muslunci a kasar faransa saboda abin da suke yi na kokarin haddasa rikici da rashin fahimtar juna tsakanin mabiya addinin musulunci da sauran mabiya addainai da suke zaune a kasar.
Bayanin ya ci gaba da cewa kasar Faransa na daga cikin kasashen nahiyar turai da suka fi yawan musulmi, ta yadda adadinsu ya zama su ne na biyu ta fuskacin yawa a kasar bayan mabiya addinin kiristanci, amma kuma duk da haka har yanzu gwamnatin kasar ba ta amince da addinin musulunci a hkumance ba amatsayin daya daga cikin addinain kasar, duk kuwea da cewa ta amince da addinin yahudanci.
1034219