Bnagaren kasa da kasa, mutanen kasar Masar sun nuna matukar damuwa dangane da yaduwar akidar salafiyya a cikin jami’ar Azhar wanda hakan yake tabbatar da babban hadarin da ke fuskantar wannan babbar jami’a ta msuulmi wadda ta bayar da gusunmwa a dukkanin bangarori.
Kamfanin dillancin labaran iqna ya habarat cewa, ya nakalto daga shafin sadarwa na yanar gizo na Al-slam cewa mutanen kasar Masar sun nuna matukar damuwa dangane da yaduwar akidar salafiyya a cikin jami’ar Azhar wanda hakan yake tabbatar da babban hadarin da ke fuskantar wannan babbar jami’a ta msuulmi wadda ta bayar da gusunmwa a dukkanin bangarori na ilimi.
Daruruwan malaman makarantu da na jami’oee a kasar Masar ne suka fito zanga zanga kan titunan birnin Al-kahira a jiya litinin inda suke kiran shugaban kasar Muhammad Mursi da cika alkawarin da ya yiwa muatanen kasar na kyautta yana yin aikin ma’aikata gwamnati. Malaman dai suna bukatar Karin albashi da kuma kyautata yanayin aikinsu, wanda sun yi ta kokarin ganin hakan ya samu a lokacin tsohuwar gwamnatin kasar amma bai yu ba. Wasu malaman sun bayyana cewa bazasu shiga aji ba a cikin sabon shekarar karatun da za’a soma a cikin mako mai kamawa, sai gwamnatin Mursi ya biya masu bukatarsu.
A makon da ya gabata ma, wasu mutanen kimani 5000 sun foto zanga zanga a birnin na al-kahira inda suka neman shugaban ya aiwatar da manufofin juyin juya halin da ya dora shi kan kujerar shugabancin kasar. Haka ma sun bukashi shugaba mursi ya salami dukkan mutanen da aka tsare a lokacin zanga zangar juyin juya halin. Wasu matasa wadanada suka jagoranci juyin da ya kai mursi kan kujerar shugabancin kasar dai sun zarshi shugaban da neman bashi dalar amurka biliyon 3.2 daga asusun lamuni ta duniya. Matasan sun bayanancewa wannan zai kara talauta kasar ne kawai.
1095227