Kamfanin dilalncin labaran iqna ya habarta cewa, ya nakalto daga shafin sadarwa na yanar gizo na NUN daga kasar Iraki cewa, a yau an gudanbar da wata gagarumar zanga-zanga domin nuna rashin amincewa da fitar da wani fim na cin zarafin addinin muslunci ta hanyar wulakanta fiyayyaen halitta manzon Allah tsira daamincin Allah su tabbata agare shi da iyalan gidansa tsarkaka da nufin tsokanar al’ummar musulmi.
kwamitin kula da ayyuka na hadin gwiwa tsakanin kasashen msuulmi masu gudanar d ayyuka da suka shafi dukkanin bangarori ya gudanar da zamansa a birnin Astaneh na kasar Qazagystan tare da halartar wakilai daga kasashe mambobi a cikinsa.
An bude wani ofishin kula da harkokin addini na kasar Kyrgystan a kasar Kuwait da nufin kara bunkasa harkokin addini da kuma kyakyawar alaka tsakanin kasashen ta fuskkar bunksa harkokin addini da ilim ga mi da al’adu a tsakaninsu kasantuwarsu mambobi a cikin kungiyar kasashen musulmi.
A cikin wanmnan makon ne wani mutum da ake kira mai bayar da fatawa na gwamnatin Saudiyya Abdulaziz Bin Abdullah Al-sheikh, ya fitar da wata fatawa daga mahangarsa ta akidar wahabiyanci da ke kafirta musulmi kansu wadanda ba su bin wannan tafarki na wahabiyanci, inda ya halasta kaddamar da kai hare-hare kan wuraren ibadar mabiya addinin kirista.
Masana da dama suka ganin a lokacin malaman addinin muslunci na hakika suke ci gaba da hankoron ganin an samu fahimtar juna tsakanin dukaknin al’ummomin duniya tare da zaman lafiya wasu daga cikin masu kiran kansu malaman addini a kasar Sudiyya suna fitar da fatawoyin halascin kai hari kan saura mutane da ba musulmi ba.
1097644