IQNA

Wani Dalili Na Kasawar AlSaud Kan Haji Shi Ne Gobara A Wani Wuri A Makka

20:21 - September 18, 2015
Lambar Labari: 3364646
Bangaren kasa da kasa, daya daga cikin dailan da wasu ke kara yin ishara da su kan kasawar gwamnatin Saudiyya danagne da daukar nauyin aikin hajji shi ne gobarar da ta tashi a jiya a babul aziziya.


Kamfanin dillancin labaran Iqna ya habarta  cewa ya nakalto daga shafin sadarwa na yanar gizo na Was cewa, gobara ta tashi a cikin wani Hotel da maniyyata  ke zaune a birnin makka mai alfarma,  na kasar saudiyya.

Shi ma kamfanin Dillancin Labarun aransa ya nakalto cewa; Gobarar ta tashi ne a cikin wani Hotel da maniyyata daga wata kasar Asiya su ke zaune a cikinsa, abinda ya sa aka killace mutane 1028 daga cikinsa.

Kawo ya zuwa yanzu babu wani rahoto da ya ke nuni da asarar rayuka sai dai wasu mutane biyu sun jikkata. Tashi gobarar a cikin birnin na makka, ya zo ne kwanaki kadan bayan da wata na’urar daga kaya, ta fado akan maniyyata da dama tare da kashe fiye da mutane dari daga cikinsu.

A kan hakan kuma rahotanni sun ce a adadin mutanen da suka rasa rayukansu sakamakon faduwar abin daular kaya ya kai 107 yayin da wasu kimanin 238 suka samu raunuka.

3364537

Abubuwan Da Ya Shafa: Mekka
captcha