IQNA

An Gudanar Da Zanga-Zangar Neman A saki Sheikh Zakzaky A Najeriya

8:37 - January 03, 2016
Lambar Labari: 3480003
Bangaren kasa da kasa, mabiya sheikh Ibrahim zakaky sun gudanar da jerin gwano a biranen Najeriya a lokacin maulidin manzo (SAW) domin neman a saki malamin da ake tsare da shi
Kamfanin dilalncin labaran iqn aya nakalto daga shafin yanar gizo na tashar Ala’am cewa, rahotannin daga Nijeriya sun bayyana cewar dubun dubatan 'yan kungiyar harkar Musulunci a kasar sun fito kan tituna da dama daga cikin biranen kasa a yau Jumu'a don kiran mahukuntan Nijeriya da su sako jagoran kungiyar Sheikh Ibrahim El-Zakzaky da suka kama a ranar Litinin din da ta gabata.
Shafin harkar Musuluncin na internet ya bayyana cewar an gudanar da irin wadannan jerin gwano da gangami ne a garuruwa daban-daban na kasar da sauran birane inda masu jerin gwanon wadanda suke dauke da hotunan Sheikh Ibrahim El-Zakzaky suka bukaci da a sako musu shugabansu da ke tsare a hannun jami'an tsaron kasar.
Shafin ya kara da cewa an dai gama jerin gwanon lafiya ba tare da faruwar wani rikici ba.
Har ya zuwa yanzu dai jami'an tsaron Nijeriyan suna ci gaba da tsare shugaban kungiyar 'yan'uwa musulmin Sheikh Ibrahim El-Zakzaky a wani wajen da ba a tantance ko ina ba ne, duk da cewa babban hafsan hafsoshin sojojin kasa na Nijeriyan ya bayyana cewar tuni sun mika Sheik El-Zakzakin ga hukumar da ta dace don gurfanar da shi a gaban kotun.
3470362
captcha