Kamfanin dilalncin labaran Iqna ya nakalto daga shafin yanar gizo na
Shafaqana cewa, harkar muslunci a Najeriya a karkashin jagorancin sheikh
Ibrahin Zakzaky ta soki kafofin yada labarai da shafukan yanar gizo na
gwamnati a kasar kan boye gaskiyar abin da ya faru.
Kamar yadda kuma
harkar ta kirayi malamai da masana a kasar da su bayyana matsayinsu kan
kisan gilla da sojojin suka yi maimakon yin shiru ko gunaguni.
Bayanin
ya ce wasu suna ta hankoron ganin sun bayyana lamarin da cewa wata
kungiya ce kawai ta wasu tsiraru har ma suna kira da a haramta kungiyar
Zakzaky alhali abin ake yi bai takaita ga yan shi’a ba kawai.
Akwai
yan sunan da kiristoci da suke shigowa ana yin taruka da su domin kuwa
suna ganin abin da ake bai ta kaita da wani bangare ba Magana ce ta
musulunci kawai.
A kan haka ne a ranar Quds yan shi’a da yan sunna
duk suna shiga wannan jerin gwano domin abin da ake yi ana kare
palastinawa ne yan sunna, kamar yadda har kiristoci suna shiga, domin
kuwa batu da ya shafi yan adamtaka.
3470655