Kamfanin dillancin labaran iqna ya habarta
cewa ya nakalto daga shafin sadarwa na jaridar Yaum Sabi cewa, Rasim
Nafis ya rubuta wata makala a matsayinsa na daya daga cikin shugabannin
yan shi’a a kasar Masar yana cewa, wasu shugabannin larabawa suna hada
kai tare da Isra’ila domin cutar da yan shia musamamn Iran da Hizbullah
da suka tsone musu ido.
Dangane da makircin da wadannan shugabanni da sarakunan larabawa suke kullawa ya bukaci taimakon bababn sakataren kungiyar Hizbullah Sayyid Hassan Nasrullah.
Haka nan kuma wannan babban masani na kasar ya aike da wani sako zuwa Sayyid Muktada Sadr na kasar Iraki, yana mai sanar da cewa mabiya tafarkin iyalan gidan amnzo a Masar zasu yi aiki da dukaknin nasihohin da ya yi musu.
Rasin Nafis ya kara da cewa matakin ma’aikatr kula da harkokin addini ta kasar Masar ta dauka na rufe masallacin Ra’asul Hussain a lokutan tarukan Tasu’a da Ashura bababn kure ne.