IQNA

Morocco Za Ta Dauki Nauyin Wani taro Mai Taken Tajwidin Kur’ani

18:10 - January 28, 2016
Lambar Labari: 3480085
Bangaren kasa da kasa, Morocco za ta dauki nauyin shirya wani babban taro mai taken tajwidin kur’ani mai tsarki a garin Kazablanka.

Kamfanin dillancin labaran Iqna ya habarta cewa ya nakalto daga shafin sadarwa na yanar gizo na Sahra Magribiyyah cewa, cibiyar kula da ayyukan addini ta kasar ce za ta dauki nauyin shirya wannan taro.

Kwamitin da zai jagoranci alkalancin wannan gasa zai kunshi mutane da suka hada da Hajir Busaq, fitatten makarancin kur’ani da ya zo na daya  akasar, da kuma sheikh Said Muslim gami da wasu daga cikin fitattun makaranta da suka shhara  akasar, su ne za su kasance alkalan gasar.

An sanar da cewa fiye da makaranta 400 za su halarci wannan gasa daga sassa na kasar Morocco.

Kamar yadda kuma aka sanar da cewa bayan kammala wannan taron gasa za abayar da kyauta ta musamman ga wadanda suka nuna kwazo, kuma kyautar za ta zama da kudi ce lakadan, kamar yadda kuma za a gayyaci wasu fitattun mutane a kasar wadanda za su gabatar da kyautukan.

A karshen wannan gasa za a girmama Allamah Muhammad Alkintawi fitaccen malamin addinin muslnci d ya bayar da gudunmawa a dukkanin bangarori na ilimin kur’ania  kasar a kasar.

3470836

 

captcha