IQNA

Taro Kan Ayyukan Kur’ani A Nahiyar A Birnin Qom

21:32 - January 30, 2016
Lambar Labari: 3480091
Bangaren kasa da kasa, an gudsanar da wani zaman taro kan ayyukan da suka shafi kur’ani mai tsarki a wasu daga cikin kasashen nahiyar Afirka wanda aka gudanar a birnin Qom.

Kamfanin dillancin labaran Iqna ya habarta cewa ya nakalto daga shafin sadarwa na yanar gizo na Qaf cewa, cibiyar Imam Hussain (AS) ce ta dauki nauyin shirya gudanar da wannan zaman taro.

Wannan taro an gudanar da shi tare da hadin gwiwa da kungiyar dalibai na Afirka, wanda aka gudanar a babban dakin taro na Warisul anbiya a birnin Qom tare da jagoranci Ma’aruf Abdulmajid daga kasar Masar.

Haji Musa Fal daga kasar Senegal tare da karamin jakadan kasar a Iran sun gabatar da wasu daga cikin ayyukan kur’ani da aka rubuta  akasar a wajen wannan taro.

Ya ce tun bayan da muslunci ya shiga nahiyar Afirka, an bayar da muhimmanci matuka wajen gudanar da ayyuka da suska shafi kur’ani, ta hanyar bude makarantu da wuraren nazari.

Ja’afar tarawure mai bincike daga kasar Mali ya gabatar da jawabinsa kan muhimman ayyukan da suka gudanar a kasar Mali a bangaren kur’ani, kamar su ma Sheikh Ibrahim daga Senegal da sheikh Ismail Bellam daga Burkina Faso, Ali Ahmad ba Mauritaniya, Hamid jalo Senegal, Ibrahim Muhammad daga Najeriya.

Wannan cibiya da ke kula da irin wadannan ayyuka da suka shafi kur’ani da ke birnin Qom, takan shirya taruka makamantan wannan, inda dalibai daga sassa na kasashen Afirka da ke karatu da wadanda suke waje sukan halarta.

3471335

captcha