
Kamfanin dillancin labaran Iqna ya habarta cewa ya nakalto daga shafin jagora cewam a lokacin da yake ganawa da daliban ya bayyana cewa: Masu fada da tsarin Jamhuriyar Musulunci suna kokari ne wajen sauya tunani na addini da juyin juya hali na matasan Iran, kawar da irin fata mai kyau da suke da shi bugu da kari kan kazar-kazar din da suke da shi. A saboda haka babbar hanyar fada da wannan makirci mai sarkakiya ita ce tarbiyyar matasa bisa tafarki na addini da koyarwar juyin juya hali, tsarkin zuciya, yin taka tsantsan, kyakkyawan fata, jaruntaka da sadaukarwa.
Jagoran juyin juya
halin Musulunci ya fara jawabinsa ne a yayin wannan ganawar da kiran matasan
zuwa ga amfanuwa da irin damar da ke cikin watan Rajab sannan kuma da watan
Sha'aban da Ramadhan inda ya ce: Wadannan watanni guda uku watanni ne na
karfafa ruhi. A saboda haka matasa wadanda suke cikin samartakarsu za su iya
amfanuwa da wannan dama wajen karfafa ruhinsu.
Daga nan kuma sai
Ayatullah Khamenei ya ci gaba da karin haske kan wasu fagage da ake samun kace
nace tsakanin Jamhuriyar Musulunci ta Iran da ma'abota girman kan duniya karkashin
jagorancin Amurka da sahyoniyawan duniya inda ya ce: 'Yancin kan kasa da suka
hada da 'yancin kai na siyasa, tattalin arziki da al'adu daya ne daga cikin
irin wadannan fagage, don kuwa manyan kasashen duniya suna fada ne da duk wata
kasa da take fada da mulkin mallakan 'yan kasashen da kuma kare 'yancin kanta.
Jagoran ya bayyana
ci gaba a matsayin daya daga cikin fagagen da ake rikici tsakanin tsarin
Jamhuriyar Musulunci da ma'abota girman kan inda ya ce: Manyan kasashen duniya
dai suna fada da duk wata kasa da take son samun ci gaban kanta ba tare da
dogaro da su ba. Don kuwa irin wannan ci gaban zai iya zama abin koyi ne ga
sauran kasashe da al'ummomi.
Jagoran juyin juya
halin Musulunci ya bayyana cewar hakan shi ne babban dalilin da ya sanya ma'abota
girman kan duniya suka shata daga wajen fada da Iran don hana ta samun wannan
kwarewar da kuma fasahar nukiliya da take da shi. Daga nan sai ya ce: Matukar
muka nuna gazawa a gaban wadannan masu tinkaho da karfi, to kuwa adawarsu za ta
ci gaba har zuwa ga sauran bangarorin ci gaba da suka hada da fasahar ilimin
halittu, Nano da sauran bangarori na ilimi masu muhimmanci da sarkakiya. Don
kuwa suna adawa da duk wani ci gaba na ilimi, tattalin arziki da wayewa da
Jamhuriyar Musulunci ta Iran za ta samu.
Ayatullah Khamenei
ya bayyana tasirin da Iran take da shi a yankin yammacin Asiya da ma duniya ba
ki daya, batun Palastinu, gwagwarmaya da kuma tsarin rayuwa ta Iran a matsayin
wani fagen da ma'abota girman kai suke da sabani da tsarin Jamhuriyar Musulunci
ta Iran inda ya ce: matukar irin tsarin rayuwa ta yammaci ta sami gindin zama a
wata kasa, to kuwa masana da masu fadi a ji na wannan kasar za su zamanto masu
mika kai ne ga siyasar ma'abota girman kai.
Haka nan kuma
Jagoran juyin juya halin Musulunci ya bayyana batun matasa a matsayin daya daga
cikin manyan fagagen da ake da sabani tsakanin Iran da manyan kasashen duniyan
inda ya ce: A halin yanzu dai akwai wani rikici da fito na fito da ke gudana
tsakanin Jamhuriyar Musulunci ta Iran a bangare guda da kuma Amurka da
sahyoniyawa a bangare guda.
Jagoran juyin juya
halin Musuluncin ya bayyana matasa daliban makarantun sakandare da na jami'oi a
matsayin sojojin wannan fito na fiton inda ya ce: A fagen wannan yakin dai ana
iya ganin wasu nau'oi biyu na dakaru sannan kuma masu akidu mabambanta, wanda
sakamakon yakin ya danganta ne da irin yanayi da tsarin wadannan sojoji biyun.
Ayatullah Khamenei
ya bayyana cewar irin wannan yakin ya fi yaki na makami hatsari, don haka yayin
da yake ishara da wasu makirce-makircen makiya a wannan bangaren ya bayyana
cewar: A wasu lokuta suna mana barazana da yaki da kawo hare-hare da ruwan
bama-bamai. Wannan wata magana ce ta wauta da kuskure. Don kuwa ba su da karfi
da kuma jaruntakar yin hakan. Amma idan har ma suka yi hakan, to kuwa za su
debi kashinsu a hannu.
Haka nan kuma yayin
da yake maganar cewa a halin yanzu ma makiyan suna ci gaba da yaki na kwakwalwa
a kan Jamhuriyar Musulunci ta Iran wanda kuma maimakon kariya ya kamata a ce
ana mayar da martani ma, Ayatullah Khamenei ya bayyana cewar: Matukar dai muna
da dakaru ma'abota riko da addini da koyarwar juyin juya halin Musulunci sannan
kuma ma'abota tunani da jaruntaka da sadaukar da kai a fagagen dagan mu, to
kuwa za a iya kirdadon sakamakon wannan yakin.
Jagoran juyin juya
halin Musulunci ya ci gaba da cewa: To amma matukar dai dakarun mu suka zamanto
masu mika kai da fadawa tarkon yaudara, masu yarda da sakin fuskar makiya,
marasa laka a jika da tunani da kuma dogaro da kai da sauransu, to kuwa
sakamakon yakin a fili yake.
Ayatullah Khamenei
ya ci gaba da cewa: A saboda haka a yayin wannan yaki na kwakwalwa, ana iya
samun sojoji masu yanayi biyu; wani soja wanda Jamhuriyar Musulunci ta Iran ta
amince da shi da kuma wani sojan wanda ma'abota girman kai suka amince da shi.
Kowane guda daga cikin wadannan sojoji yana iya taka rawa wajen tsara sakamakon
yakin.
Jagoran juyin juya
halin Musulunci ya ci gaba da cewa: Kasashen yammaci musamman Amurkawa suna
kokari ne wajen mayar da matasan Iran su zama wasu matasa marasa imani, marasa
jaruntaka, marasa laka a jika, marasa kyakkyawar fata da kuma dogaro da makiya,
to amma tsarin Musulunci yana kokari ne wajen tarbiyyantar da matasa wajen zama
kishiryar abin da ma'abota girman kai suke son su zama.
Don haka sai yayi
kira zuwa ga kula da kuma ba wa matasan tarbiyyar da ta dace, kamar yadda kuma
ya kirayi jami'an ma'aikatun ilimi da tarbiyya ta kasar Iran da su sauke nauyin
da ke wuyansu a wannan bangaren.
Jagoran juyin juya
halin Musulunci ya bayyana yanayin da matasan kasar Iran suke ciki a matsayin
yanayi da ke cike da fata mai kyau inda ya ce: Duk kuwa da wasu abubuwa da ake
da su masu kautar da matasa daga kan tafarki madaidaici bugu da kari kan irin
fagage na kiyayya da ake yiu da su, to amma a halin yanzu muna da matasa
ma'abota imani, masu kusaci da Ubangiji, masu tattaki ranar arba'in, ma'abota
karatun Alkur'ani, I'itikafi kana kuma ma'abota tsayin daka a fagage daban
daban na juyin juya halin Musulunci, wanda abin godiya ce ga Allah Madaukakin
Sarki.
Ayatullah Khamenei
ya bayyana samuwar irin wadannan matasan a kasar Iran a matsayin wani lamari
mai girman gaske. Har ila yau kuma yayin da yake jaddada cewa bayan shekaru 37,
har ya zuwa yanzu ma'abota girman kai sun gagara kawar da Jamhuriyar Musulunci
ta Iran ko kuma su hana ta ci gaba, Jagoran ya bayyana cewar: Duk da barazana a
aikace da kuma farfagandar da ake yadawa, amma a halin yanzu kungiyar Hizbullah
ta kasar Labanon ta tabbatar da matsayinta a duniyar musulmi. A saboda haka yin
Allah dai da ita da wata lalatacciyar gwamnati ‘yan amshin shata wacce aka bar
ta a baya, ba shi da wani muhimmanci.
Haka nan kuma yayin
da yake ishara da shan kashin da haramtacciyar kasar Isra'ila ta sha a yakin
kwanaki 33 da kuma kwatanta irin wannan nasarar da shan kashin da sojojin kasashen
larabawa uku a gaban sojojin haramtacciyar kasar Isra'ilan, Jagoran juyin juya
halin Musulunci ya bayyana cewar: Kungiyar Hizbullah da matasanta muminai, har
ya zuwa yanzu suna ci gaba da haske tamkar hasken rana sannan kuma sun zamanto
abin alfaharin duniyar musulmi.
Ayatullah Khamenei
ya ci gaba da cewa: Mai yiyuwa ne gaskiya ta fuskanci matsaloli da wahalhalu,
to amma daga karshe dai za ta yi nasara.
Ayatullah Khamenei
ya bayyana tsayin dakan dakarun gaskiya a matsayin sharadin na asali na nasarar
gaskiya a kan karya inda ya ce: Gaskiya da hakika tana tare da wadannan
matasan, kuma da yardar Allah wata rana za ta zo da matsalolin da ake fuskanta
za su kawu, sannan kuma wadannan matasan za su kasance a sama.
Kafin jawabin
Jagoran juyin juya halin Musulunci sai da wakilin Jagoran juyin juya halin
Musulunci a kungiyar hadin kan daliban Musulunci Hujjatul Islam wal muslimin
Hajj Ali Akbari ya gabatar da jawabinsa dangane da ayyukan da kungiyar ta ke yi
wajen tarbiyyar daliban makarantu.
Har ila yau kuma
wasu dalibai biyu daga cikin membobin kungiyar su ma sun gabatar da jawabinsu
inda suka yi Karin haske dangane da irin matsaloli da kalubalen da suke
fuskanta.