Kamfanin
dillancin labaran Iqna ya nakalto daga shafin sadarwa na yanar gizo na Baffalo
News cewa, Shahnaz Bat tsohuwar shugabar kungiyar musulmi mata akasar Amurka ta bayyana cewa, idan aka yi la’akari
da abin da ke cikin kur’ani yana ishara da Maryam (AS)
Ta ce ko shakka babu muslunci yana girmama Maryam (AS) da kuma danta annabi Isa (AS), idan aka yi la’akari da yadda muslunci yake girmama su to za a fahimci cewa ba shi da wata husuma da wani addini.
A wannan zaman taron dai an asamn halartar mabiya addinan kirista da kuma na muslunci, inda ake gabatar da jawabai na hadin kai da fahimtar juna atsakaninsu.
Musulmin kasar dai suna fuskantar matsaloli tun bayan da yabn ta’adda suka fara kaddamar da hare-hare da sunan addinin muslunci, wadanda suke dauke da akidar ta’addanci.