IQNA

Obama Ya Isar Da Sakon Taya Musulmi Murnar Shiga Watan Ramadan

23:53 - June 06, 2016
Lambar Labari: 3480483
Bangaren kasa da kasam shugaban kasar Amurka Barak Obama ya isar da sako ga dukaknin usulmin kasar Amurka na taya su murnar shiga cikin watan azumin Ramadan.

Kamfanin dilalncin labaran Iqna ya habarat cewa ya nakalto daga shafin sadarwa na yanar gizo na Associated Press cewa, Obama ya isar da sakon nasa kamar yadda yasaba a kowace shekara, tare da bayyana cewa wannan wata lokaci na ibada da tsarkake zuciya da kuma yin yafiya.

Oabam ya ce Amurka kasa ce wadda ta hada mabiya addinai daban-daban da suka hada da musulmi,kuma ana kare hakkokinsu kamar yadda ake kare hakkin kowane dan kasa, domin kuwa a cewarsa kasarsa kasa ce mai girmama hakkin dan adam.

Wannan furuci na Obama dai ya zo a daidai lokacin da dan takarar shugabancin kasar Amurka a karkashin inuwar jam’iyyar Republican Donald Trump yake ta kara bayyana matsayinsa nag aba ga addinin muslunci da kuma musulmi.

A cikin yan lokutannan dai sakamakon hare-haren ta’addancin da masu dauke da akidar kafirta musumlmi suke kaiwa a cikin kasashen yammacin turai, kyaar addinin muslunci ta karu matuka.

Gwamnatin Obama tana a sahun gaba wajen sayar da makamai ga kasashen larabawan yankin gabas ta tsakiya da suke yada akidar ta’addanci.

3504306

captcha