Kamfanin dillancin labaran kur’ani na Iqna ya habarta cewa, a daidai lokacin da ake gudanar da azumin watan Ramadan mai alfarma, ya kirkiro da wani shiri na karatun kur’ani wanda za a iya kada kuri’a domin zaben daya daga cikin makaranta ta hanyar shafuka 16 da yake watsa labarai a cikin harsuna na duniya daban-daban.
Wannan shiri dai zai gudana ne a matakai 5, inda yanzu ake a mataki na farko, kuma makaranta 25 ne za su shig cikin shirin, daga karshe za a fitar da wanda ya samu ra’yoyin jama’a, inda IQNA za ta ba shi kyauta ta musmman.
Kuma wannan jin ra’ayin jama’azai hada dukkanin sauran shafuka na harsunan waje da wannan kamfanin dullancin yada labarai na kur’ani ke watsa labaransa.
Wnnan dais hi ne karon farko da ake gudanar da wani shiri irin wannan, wanda zai hada fitattun makaranta na kasar Iran, wadnda suka hada da Ahmad Abulqhasemi, Muhammad Redha pour Zargari, Hamid Shakernejad, Saeed Tusi, Mansur Qhasri Zadeh, wadanda suke da bukata, bayan sauraren karatun wadannan makaranta, za a iya zaben wanda ake tilawarsa tafi burgewa.
Domin zabar wanda ake so sai leka shafin Iqna:
Ahmad Abulqhasemi aya ta 16 zuwa 31 surat Maryam
http://iqna.ir/files/fa/news/1395/3/25/173640_987.mp3
.................................................................................................
Muhammad Redha pour Zargari aya ta 21 zuwa 25 surat Ahzab, 1 zuwa 15 surat Qamar
http://iqna.ir/files/fa/news/1395/3/25/173647_100.mp3
.................................................................................
Hamid Shakernejad aya ta 31 zuwa 37 Al Imran
http://iqna.ir/files/fa/news/1395/3/25/173659_885.mp3
....................................................................................
Saeed Tusi aya 18 zuwa 28 Hashr
http://iqna.ir/files/fa/news/1395/3/25/173438_292.mp3
.....................................................................................................
Mansur Qhasri Zadeh aya 41 zuwa 58 surat Maryam
http://iqna.ir/files/fa/news/1395/3/25/173675_670.mp3
Za a gudanar da mataki na biyu a cikin wannan wata.