Kamfanin dilalncin labaran iqna ya nakalto daga shafin yanar
gizo na jaridar Manama Post wadda ta rubta a shafinta na yanar gizo cewa,
masarautar mulkin mulukiya ta Al Khalifa akasar Bahrain tana sayen wasu daga
cikin 'yan jaridar kasar da take da alaka da su, domin bata sunan wasu fiattun
mutane da al'ummar kasar ke ganin kimarsu, sakamakon mahangarsu ta siyasa, ko
kuma banbancin fahimta ta mazhaba.
Bisa ga rahoton wannan jarida masautar ta Bahrain ta ware makudan kudade domin
gudanar da wannan aiki, dukkanin mutanen da ake nufin bata sunansu ta wannan
hanyar kuwa manyan malaman addini ne na mabiya mazhabar shi'a a kasar, sai kuma
fitattun 'yan siyasa da kuma shugabannin cibiyoyin farar hula da na kare hakkin
bil adama a kasar, matukar dai mabiya mazhabar shi'a ne.
Mahukuntan Bahrain wadanda 'yan sunna ne da turawan mulkin mallaka na Birtaniya
suka mika wa ragamar mulkin kasar kafin ficewarsu, sun jima suna daukar matakan
gallazawa ga mabiya mazhabar shi'a a kasar wadanda su ne fiye da kashi 85 cikin
dari na al'ummar kasar, inda lamarin ya kara tsananta a baya-bayan nan,
sakamakon kran da suke na a yi adalci a cikin sha'anin mulki da siyasa, ta
hanyar kafa majalisar dokoki wadda al'umma za su zaba da kansu, maimakon yadda
ake yi yanzu, inda sarki ne da kansa ke nada 'yan majalisa, kuma su aiwatar da
abin da ya ga dama a cikin majalisar.
Wasu daga cikin kafofin yada labarai na sarakunan mulkin kama karya daga cikin
kasashen larabawan yankin tekun fasha, da suka hada da na Qatar, Saudiyya da kuma
hadaddiyar daular larabawa, suna yin aiki tukuru wajen yada wanann manufa ta
masarautar Bahrain.
Matkin baya-bayan nan da masarautar mulkin kama karya ta Bahrain ta dauka shi
ne rusa jam'iyyar Alwifaq, jam'iyyar siyasa mafi girma a cikin dukkanin kasashen
larabawan yankin tekun fasha, tare da janye izinin zama dan kasa daga kan
Ayatollah Sheikh Isa Kasim babban malamin addi mafi karfin fada aji a kasar.