IQNA

Hadin Kai Tsakanin Mabiya Addinan Musulunci Da Kiristanci

16:50 - October 30, 2016
Lambar Labari: 3480892
Bangaren kasa da kasa, mabiya addinan muslunci da kiristanci a birnin New bury sun gudanar da taro na hadin kai a tsakaninsu.
Kamfanin dillancin labaran kur'ani na iqna ya habarta cewa, ya nakalto daga shafin sadarwa na yanar gizo na New Bury Taday cewa, a raar Juma'a da ta gabata mabiya addinin kirista daga majami'ar birnin sun je masallacin Juma'a, kamar yadda su ma musulmi sun je majami'a sun zauna a lokacin kiristoci ke ibadarsu.

Poul Covan shi ne shugaban majami'ar Cent George da ke birnin wadda tana daya daga cikin manyan majami'un kistoci a kasar Birtaniya, ya ziyarci masallacin Juma'a a lokacin sallar Juma'a kuma an yi sallar tare da shi.

Covan ya ce akwai abubuwa da dama da suke faruwa a duniya wadanada suke jawo tsoro da rashin yarda da juna, wadanda ya kamata su kawo karshe, domin musulmi da kiristoci ba abokan gaba ba ne, dukkaninsu mabiya addinai ne da aka safkar daga sama.

Ya ce za su ci gaba da yin kokari domin ganin an samu kyakyawar dangata tsakanin kiristoci da musulmi, ta yadda kiristocin da ke tsoron musulmi ko suke yi musu wani kallo su gane cewa ba haka musulmi suke ba.

Babban malamin kiristan ya ce tun bayan kisan da aka yi wa malamin kirista a Faransa a kwanakin baya, wasu kiristoci a kasashen turai sun dauki karan tsana sun dora kan msuulmi, alhali wadanda suka aikata wannan danyen aiki ba suna wakiltar dukkanin musulmi ba ne, bil hasali ma musulmin duniya sun yi Allawadai da hakan.

3541872


captcha