IQNA

23:52 - December 25, 2016
Lambar Labari: 3481068

Daurin Shekaru 4 A Gidan Kaso Kan Mai Wulakanta Kur'ani

Bangaren kasa da kasa, wata kotu a birnin kazablanka na kasar Morocco ta daure wata mata mai wulakanta kur'ani shekaru 4 a gidan kaso.

Daurin Shekaru 4 A Gidan Kaso Kan Mai Wulakanta Kur'ani

Kamfanin dillancin labaran kur'ani na iqna ya habarta cewa, ya nakalto daga shafin sadarwa na yanar gizo na hespress.com cewa, kotun ta Kazablanka ta yanke hukuncin ne a kan wannan mata bayan da ta wulakanta kur'ania acikin wasu masallatai a yankin Lisasafaha tare da tara da dirhami 500.

Wannan mata dai wadda ta kai kimanin shekaru 40 da haihuwa, tana shiga cikin masallatai ne a lokacin da ta lura da cewa ba a ganinta, sai ta keta kwafin kur’anai da ke cikin masallatan.

Ta yi hakana wasu masallati amma ba a iya gano ta ba, sai a lokacin da ta yi hakan a masallacin Lisasafa, inda limamnin masalacin da kansa ne ya lura da cewa ta shiga bangaren mata bayan kammala sallar isha’I, kuma alokacin babu kowa a ciki, bayan ta fita sai aka ga an yaga kur’anai a da ke wurin.

Yanzu haka dai an kame ta kuma an gurfanar da ita agaban kuliya, inda kotu ta yanke mata hukuncin daurin shekaru hudu a jerea gidan kaso, tare da biyan tara, an yi hakan ne domin ya zama darasi gad k wani mai tunanin yin irin aikin da ta yi na keta alfarmar kur’ani mai tsarki.

3556548/4



captcha