IQNA

Ayyukan Kur'ani Da Iran Ke Gudanarwa A Afirka Ta Kudu

21:00 - August 09, 2017
Lambar Labari: 3481782
Bangaren kasa da kasa, a yau ne za a watsa wani shiri dangane da ayyukan da jamhuriyar muslunci ta Iran take gudanarwa a bangaren kur'ani a kasar Afirka ta kudu a tashar Rasad.
Kamfanin dillancin labaran iqna ya bayar da rahoto n cewa, bangaren hulda da jama'a na cibiyar yada al'adun muslunci ta kasar ya sanar da cewa, Fallah Pisheh shugaban ofishin yada al'adun muslunci a Afirka ta kudu ya ce, a yau ne za a watsa wani shiri dangane da ayyukan kur'ani da Iran take gudanarwa a Afirka ta kudu a tashar Rasad ta kur'ani kai tsayi.

A Larabar da ta gabata ma an saka wani shiri makamncin haka tare da shugabannin ofisoshin yada al'adun muslunci na Iran a kasashen Girka Ali Muhammad Helmi, Ali Asgar Amiri na Bosnia, Ali Bakhtiyari Uganda, Abdul Ridha Saifi, da kuma mataimakin shugaban ofishin akasar Indonesia.

Dukkaninsu sun gabatar da bayanai da kuma nuna irin ayyukan da ake gabatarwa ta fuskacin ayyukan kur'ania kasashen da suke wakiltar jamhuriyar musulunci ta Iran.

3628490


captcha