IQNA

Martanin Dalai Lama Kan kisan Musulmi A Mayanmar

16:53 - September 11, 2017
Lambar Labari: 3481885
Bangaren kasa da kasa, jagoran mabiya addinin buda na Tebet Dalai lama ya bayyana rashin jin dadinsa dangane da kisan da ake yi wa msuulmi 'yan kabilar Rohingya a kasar Myanmar.
Kamfanin dillancin labaran iqna ya bayar da rahoton cewa, jaridar Telegraph ta bayar da rahoton cewa, Dalai lama ya bayyana cewa, duk wani dan addinin buda da yake da hannu a kisan musulmi a Myanmar ya sake yin tunani kan addininsa.

Ya ce ko shakka babu addinin buda bai yarda da kisan jama'a ma ba gaira ba sabar, domin kuwa musulmi 'yan kasar Myanmar 'yan kabilar Rohingya babu wani laifi da suka yi wa wani balantana a kasha su haka kisa na wulaknci da tozarci.

Haka nan kuma ya kirayi firayi minister kaar ta Myanmar Suu Kyi da gaggauta daukar matakin ganin an dakatar da wannan mummunan aiki da ak eyia kasar da sunan addinin buda, kuma su samo hanyoyin yin sulhu da zaman lafiya atsakanin dukkanin al'ummar kasar.

Dalai Lama ya ce hakika hankalinsa ya tashi matuka dangane da kisan da ake yi musulmi Myanmar, da kuma yadda ake tozarta su da ci musu zarafi, inda yace hakaki na yana cikin bakin maras misiltuwa akan wannan mummunan aiki.

Tun daga lokacin da 'yan addinin buda tare da sojojin gwamnatin Myamanr suka fara yin kisan kiyashi a kan musulmi a kasar kimanin makonni uku da suka gabata, yazu yanzu an kasha dubai tare da raunata wasu, wasu kuma sun tsere sun bar gidajensu.

3640611


captcha