IQNA

'Yan Shi'a A Tanzania Sun Gudanar Da Zaman Makokin Imam Hussain (AS)

16:56 - September 26, 2017
Lambar Labari: 3481935
Bangaren kasa da kasa, mabiya mazhabar iyalan gidan manzon Allah (SAW) sun gudanar da zaman makokin shahadar Imam Hussain (AS) a masalacin Alghadir da ke Darussalam.
Kamfanin dillancin labaran iqna ya bayar da rahoton cewa, a jiya an
gudanar da zaman makoki a birnin Darussalam an kasar Tanzania, domin juyayin shahadar Imam Hussain (AS).

Sheikh Jalal shi ne shuagaban makarantar Imam Sadiq (AS) kuma shi ne ya gabatar da jawabia wurin tare da halartar mabiya tafarkin manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi da iyalan gidansa tsarkaka.

An gabatar da jawaban ne a cikin harsunan farisanci da larabci kasantuwar cibiyar tana gudanar da wani shiri na koyar da harshen farisanci a wurin ga dalibai da dama, wadanda a halin yanzu suna fahimtar harshen.

Shugaban karamin ofishin jakandancin Iran tare da wasu daga cikin malamai sun halrci wurin gudanar da wannan taron makoki.

3646495



captcha